WURIDINDA ZAKAYI DOMIN MALLAKAR YARINYA KO SAURAYI

 

WURIDINDA ZAKAYI DOMIN MALLAKAR YARINYA KO SAURAYI

Assalamu alaikum Warahamatullahi Ta'ala Wabarãkatuhu mabiya wannan shafin namu mai tarin albarka Na Shehu Yaseen Muhyiddeen Ngibrima, Muna yiwa kowa fatan alkhairi tare da roƙon Allah ya biya mana buƙatummu duniya da lahira.

A yau dai zamu yi bayani ne akan yadda zaka / zaki mallaki wanda kakeso kokuma wanda kikeso, ma'ana kasa ko kisa Allah ya juyo da hankalinsa da ra'ayinsa akanka ko akanki ta hanyar addu'a zalla, ta yanda zai kasance yana qaunar ki sosai yakasance baya son kowa sai ke, idan ma yana yimaki wulaqanci ne afarko kokuma yana jamiki aji to da yardar Allah zai daina duk abunda yakeyi wanda bakya jin daɗinsa, ga yanda aikin yake👇

Dafarko dai shi duk wanda kakeso to abune mai muhimmanci agurinka, abu ne mai daraja indai kanason mutum to bazakaso ka rasashi ba, Allah ya haliccemu kuma ya halicci soyayya atsakanin mace da namiji, duk inda yakasance maza da mata suna ganin juna to dolene soyayya zata shiga zuciyarsu, sannan kuma addu'a akan wanda kakeso abune mai wahala sosai domin yanada matuqar wahalarwa Idan baka dage ba sosai, amma yin hakan dolene ga duk wani mutum mai hankali kuma wanda yake neman zabi da albarkar Allah acikin soyayyarsa, kuma juyoda hankalin mutum sai an dage sosai, amma kuma ni na musamman ne domin bazan gaya maku abunda bayada amfani ba domin kubata lokacinku, idan nayi haka banyi muku adalci ba ,,addu'a irin wannan sunada yawa sosai, amma kuma na tsaya na zaɓo wadda tafi kowace qarfi acikin addu'o'in kuma tafi kowace saurin kaamawa, domin kusamu sauqin biyan buqata da kuma saurin riskar waɗanda kukeso arayuwarku, ga yanda aikin yake👇

Shi wannan aiki aiki ne na wuridi, ba rubutu bane ba laqani bane ko wani abu, kuma ana yin wuridin ne na zama uku (3), ma'ana kwana uku ko huɗu (4) kokuma kwana shida (6), ana son yakasance kanada cikakken tsarki a lokacinda zaka yi wannan addu'ar, sannan kuma zaka yi addua'ar ne a zama uku kokuma hudu, kokuma zama shida, ma'ana ba'aso addu'ar azauna yinta fiyeda zama shida acikinta, kaga kenan aduk zama ɗaya at least za'a yi wannan addu'ar dubu biyu (2000) kenan, anaso a shafa tirare mai qamshi sosai a duk lokacinda za'a fara yin wannan wuridin, bayan kayi alwala kazauna sai kafara yin waɗannan addu'o'in 👉 Istigfari qafa ɗari (100), Salatin Amnabi qafa ɗari (100), La ilaha illallahu qafa ɗari (100), bayan ka gama sai kayi niyyar abunda kake so Allah yabaka (wadda kake so ko wanda kike so) sannan sai kafara ko kifara wuridin wannan ayar👇

Note (AKULA): A tabbatar an karanta wannan Addu'ar yanda aka ganta fa, kar a canza komai acikinta, abaibai ake karanta wannan ayar:

 “laqaadirun raj'ihi alã innahu”

Qafa dubu goma sha biyu (12,000),

Kar a manta za'a iya yin zama shida acikinta, za'a iya raba wannan addu'ar zuwa kwana shida ko zama shida (6), idan aka kammala duka wuridin dubu goma sha biyun sai ayanka kaza ayi sadaka, kokuma asayi ɓararrar gyada kamar ta naira ɗari biyu (200) wadda ba'a soya ba sai ajiqata da ruwa asaka sugar sosai acikin gyaɗar, idan Ta jika sai ayi rami azuba ruwan gyaɗar, ƴaƴan gyaɗar kuma sai arabawa almajirai da qananan yara sadaqa, amma fa idan so samune anfiso ayi yanka ayanka kazar ayi sadaka, amma idan hakan baisamuba sai ayi da gyaɗar, idan anyi haka shikenan Insha Allahu asa ido aga ikon Allah, indai anyi wannan wuridin dai dai kuma anyishi acikin Ikhlasi to za'a dace Insha Allahu.

To wallahi da yardar Allah mahalicci mai biyan buqata idan kayi / kikayi wannan aikin dana bayar asama, ko wanene mutun bi'iznillahi sai ya soki, ko wacece da izinin Allah sai tasoka soyayya ta haqiqa ba jeka nayika ba.

Wannan sirrin mujarrabi ne domin angwada Shi ba yauba ba gobeba kuma yayi aiki, kuma ina so ku jaraba kuzo kubani labari kokuma ku kirani kuyi godiya, Allah yasa kudace kuma Allah yasa ayi aiki lafiya kuma asamu biyan buqata asamu ijaba acikin aikin, Allah yazaɓamana abokanan rayuwa nagari Allah ya yayemana damuwarmu yabamu zuri'a ɗayyaba amin.

Domin neman qarin bayani kokuma masu neman ayi musu wannan aikin ko wani aiki na kiranye ko mallaka mai qarfin gaske, ko matsalar rashin lafiya, ko wacce takeson yin aure ko maganar kasuwanci, kokuma aiki wanda ya shafi rayuwarsu kokuma lafiyarsu ko mu'amalarsu da koma wane irin aiki sai su tuntubeni akan numbobina kokuma akan WhatsApp a wadannan numbobin nawa👇

Domin kira, 08105966742

Domin Whatsapp Za'a Iya Amfani Da Wannan Linki Ɗin.

https://wa.me/2347060916899

Ga link na Whatsapp group din mu:

 https://chat.whatsapp.com/IKbFo1GbztC9sCZIEffHhn

Email address:

Yasinmuhyiddeengibrima@gmail.com 

Sannan muna yin ko wanne irin aiki da yadda ALLAH, Alhamdulillahi

Alhamdulillah

Next Post Previous Post
No Comment
Add Comment
comment url